4 Afirilu 2021 - 07:09
​Iran: Yawan Wadanda Suke Rasa Rayukansu Sanadiyyar Cutar Korona Ya Na Kara Yawa Bayan Tafiye-Tafiyen Karshen Shekara

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Iran ta bada sanarwan cewa yawan wadanda suke rasa rayukansu sanadiyyar cutar korona ya fara yawa bayan tafiye-tafiyen na hutun karshen shekara da mutane suka yi a kasar.

ABNA24 : Kamfanin dillancin labaran Iran Press ya bayyana cewa ma’aikatar ta bada rahoton mutuwar mutane 117 sanadiyyar cutar a jiya jumma, wanda shi ne adadin da ya haura 100 a karon farko cikin watannin da suka gabata.

A halin yanzu dai jimillar mutane 62,876 suka rasa rayukansu sanadiyyar cutar tun bayan bullarta a farkon shekara ta 2020 a kasar. Sima Sadat Lari kakkain ma’aikatar kiwon lafiyar ta kasa ta bayyana cewa mutane 11,660 ne suka kamu da cutar a jiya jumma’a kadai, sannan 1,330 daga cikinsu suna jinya a asbitocin kasar.Ya zuwa yanzu dai jimillar mutane 1,908,974 suka kamu da cutar sannan 1,633,949 suka warke.

342/